27/04/2026
Daga Coach Ahmad 👇👇👇
ILLAR DA AKA YI WA MATASAN AREWA
A lokutan baya, idan matashi ya fara tasowa, sai a ce masa ya tafi kasuwa ya bar neman ilimi saboda neman kudi. A hankali, wannan ya zama dabi’a a Arewacin Najeriya.
Ta wannan hanyar ne matasa da dama s**a rasa damar bunkasa hazakarsu. Har ta kai ga cewa ‘yan Kudu s**a yi mana nisa sosai a fannin technology da kasuwancin zamani.
Yanzu muna gani da idonmu yadda fasaha ke shigowa cikin kasuwancinmu, amma saboda rashin shiri, da yawa daga cikin ‘yan kasuwa suna fuskantar matsaloli, wasu ma harkokinsu sun durkushe.
Ana magana cewa Aliko Dangote yana saka jari a kasuwannin zamani kamar stock market, amma mu kuma an takaita mana tunani. An koya mana cewa idan mun gama secondary school, kawai mu tafi kasuwa ba tare da bunkasa iliminmu ba domin mu kawo sauyi a noma da kasuwancinmu.
Wannan babbar matsala ce.Idan ba mu farka ba, nan gaba za a bar mu a baya.
Babban kalubalen shi ne:
1) Wasu daga cikinmu ba su iya bude WhatsApp ba
2) Wasu ba su iya amfani da Play Store ba
3) Wasu ma ba su iya bude Facebook ba
To ina batun sarrafa technology? Ina kuma batun amfani da AI wanda shi ne gaba na duniya?
SHAWARA:
Lokaci ya yi da za mu gyara.
a) Mu dawo hanya madaidaiciya
b) Mu koma makaranta
c) Mu hada ilimi da kasuwanci
d) Mu yi amfani da iliminmu wajen kawo cigaba a al’ummarmu
゚